New Post

Friday, 17 March 2017

SHAUKIN SO

✨✨✨✨✨✨✨✨✨
     ❤ *SHAUKIN SO*🌷
✨✨✨✨✨✨✨✨✨
      ✨✨✨
         ✨✨
            ✨

NA

*ABDULAZIZU AAJ*✍
            DA
*NEERATLURV*😍


Via O.H.W📚

          *26-30*

  _*cigaban lbr*_

Abdul ya koma garinsu na bauchi da yake daman gurin kanen mahaifinsa ne ya je, a can ne ya hadu da Mama wato garin kano, bayan Abdul ya dawo gidansu bai bari yayi kwana koda daya bane ya je ya sanar da mahaifinsa zancen Mama, ya kuma gaya masa dukkanin abinda ya shafi rayuwarta. Mahaifin Abdul yana matukar son abdul hakan yasa yake masa komai yake so, bayan yaji zancen Abdul ya kuma amince da abindaAbdul ya zo masa dashi.
Mahaifin Abdul ya tura kannensa wurin neman auren d’ansa Abdul da Mama. Bayan iyayen Abdul sun je gidansu Mama neman auren Mama, mahaifinta yayi musu walakanci sosai wanda kare ma bazai daukaba, yakuma sanar dasu kancewa baxai bada auren ‘yarsa ga wani yareba face yaren FAKANCI.”

 “ bayan sun dawo sun sanar da mahaifin Abdul abinda duk ya faru shima kuma ya nuna bakin cikinsa sosai da faruwar wannan al’amari tare da sanar da Abdul halin da ake ciki, hade da Jan kunnnsa kan yaxama dole yafita hanyan Mama inyanason farincikinsa, toh kawai Abdul yace amma bayajin zai iya.”
Abdul yaje dakinsa ya kwanta yana jimamin wannan al’amari, yana kwance ya dauko wayarsa ya kira masoyiyarsa Mama, kamar jira take yana bugawa sau daya wayar tayi ringing Mama ta dauka, tana dauka abdul yaji ta tana shesshekar kuka, cikin yanayin damuwa shima yace da ita “Tawa me yasa kike kuka?” muryarta a sarkake tace “me zaisa bazan yi kuka ba, daman zuwan wannan rana nake gudu a rayuwata, da ganin wannan rana dama mutuwa tazo ta daukeni kafin zuwanta…” “kidaina fadan haka, ai ni bana tunanin rabuwa dake saboda nasan rabuwa dake abune wanda bazai yuyu ba, tunanina kawai ya za’ayi mu kasance a tare, ni da ke tamkar haduwar gulbi da teku ne wadanda ba zasu taba rabuwa ba” Abdul ne ya katsewa Mama Magana tare da fadan haka, sai kuma ita tace “raba rayuwata da kai tamkar raba kifi ne da ruwa wanda babu tabbacin rayuwarsa idan ya fito ruwa, haka nima idan akace a raba zuciyata da soyayyarka to tabbas zan iya mutuwa” sai yayi murmushin karfin hali yace “ai rabuwa takan zo ne ga masoya a bisa kaddara, mu kuma tamu soyayya babu kaddarar rabuwa acikinta, kaddara daya itace mutuwa, amma raba zukatan mu da soyayyar junan mu abune wanda bazai yuyu ba, wallahi Mama ko ni akace na ciro soyayyarki acikin zuciyata bazan iya ba, ballai wani daban ya cireta, gangar jikin mu ne suke son rabawa amma bazasu iya raba soyayyarmu ba, ki daina zubar da hawayenki domin kuwa ni naki ne” sai tace

  “wannan dalilin yasa zuciyata take alfahari dakai, domin kaine ka zamo sa gudun duk wani bakin ciki da ya tunkaro zuciyata tareda maye farin ciki a gurbin bakin ciki, tabbas kafin nayi waya dakai zuciyata tafarfasa take tamkar ana gobara acikinta, amma yanzu sakamakon jin kalaminka da tabbacin zaka kasance dani komai tsanani. Lokaci daya naji zuciyata ta dawo tamkar ba wani abu da yake damunta tare da bayarda jin dadi ga sassan jikina yanzu banjin komai yana damuna” “kawo wayar nan ‘yar iska” Mahaifinta ne yayi mata wannan Magana cikin tsawa lokacin da ya tarar da ita tana waya da Abdul, ya karbe wayarta tare da cigaba da yimata fada daga karshe yayi mata sharadin kada ta sake fita waje.

“Jikin Abdul ne yayi sanyi lokacin da yaji sautin mahaifinta yayi wannan Magana tare da karbe waya ya kashe. Lokaci daya Abdul yaji ya kasa tsayuwa da kafafunsa ya shiga tunani iri-iri, sai kuma ya tashi ya yunkura zuwa waje don tunkarar garinsu Mama, yana kai bakin kofar dakinsa ya tarar da mahaifinsa a tsaye, sai mahaifinsa ya dubesa cikin harara yace “bani makullin motar nan” ya mika hannunsa zuwa ga Abdul, cikin sanyin jiki Abdul ya dauko makullin motar daga cikin aljihunsa ya bashi, sai kuma Babansa ya sake cewa.”

    “yanzu sai kaje duk gidan uwar da zaka je, kuma ina mai shaida maka cewa daga yau babu kai babu zuwa ko ina, idan kuma ka fita, idan ranka dubu ne sai dukansu sun bace” sai yayi tsaki ya juya ya tafi.”

 “ Abdul ya koma cikin daki yana zubar da hawaye tare da sake kiran Mama amma yaji wayarta a kashe, lokaci daya ya shiga damuwa, a haka ya kasance cikin damuwa da bakin ciki.”

“Tsakanin Abdul da Mama kowa ya kasance cikin bakin ciki da damuwa tare da tunanin halin da dayansu yake ciki, amma babu mai jin labarin wani saboda kowa yana gidan an tsare”.

   “cikin haka kawun Abdul na kano ya dawo bauchi da zama duka.”

    “haka rayuwarsu taci gaba da gudana cikin yanayin bakin ciki da rashin jin dadi, duk Abdul yashiga wani yanayi, ga gidansu an daukemasa wuta, aunty asiyace kadai ke kwantar masa hankali da sasa cin abinci dan tana matukar tausayawa sirkinta Abdul."

   "Haka Mama duk gidan jiyane itama....


Daga alkalamin:-

*NEERATLURV*😍
        &
*ABDULAZIZU AAJ*✍
  (Na England..)

_Dedicated to Maryam (Mama)_❣

No comments:

Post a Comment

Popular Posts